Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi

Ministan ‘yan sandan kasar Afirka ta kudu, ya ce, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na cewa an yi wa fararen fatar kasar kisan

Ministan ‘yan sandan kasar Afirka ta kudu, ya ce, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na cewa an yi wa fararen fatar kasar kisan kiyashi a yayin ziyarar da shugaban kasar Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa ya kai.

A yayin ganawar da ya yi da shugaban kasar Afirka ta kudu, shugaban kasar Amurka ya kunna wani faifen bidiyo da a ciki  aka  nuna  gicciye a gefen hanya domin tunawa da fararen fata manoma da aka yi wa ksian gilla.

Ministan ‘yan sandan kasar ta Afirka ta kuku Senzo Mchunu ta cewa; Wadannan gicciyen ba su nuni da cewa suna akan kabarurruka ne, ko wani wuri na tunawa da matatu, an Sanya su ne a 2020 domin tunawa da dukkanin manoman da aka kashe a fadin kasar ta Afirka ta kudu.

Har ila yau, ministan ‘yan sandan na kasar Afirka ta kudun ya kuma kara da cewa; ‘yan fashi da makami sun kashe wasu ma’aurata manoma a cikin gonarsu, yana mai kara da cewa; Abinda Trump ya yi shi ne murguda wancan labarin da kirkirar abinda ya kira; “Kisan Kiyashi.”

Mchunu ya kara da cewa; kasar Afirka ta kudu tana girmama mutanen Amurka da shugaban kasarta, amma ko kadan ba ta  girmama kirkirarren labarin; Kisan Kiyashi.”

Amurka ta dauki wannan matakin ne dai a kan Afirka Ta Kudu saboda ta kai karar HKI akan kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments