Adadin ‘Yan Jaridar Falasdinu Da Suka Yi Shahada Sun Karu Zuwa 226 Tun Bayan Fara Kisan Kare Dangi A Gaza

Adadin ‘yan jarida wadanda suka yi shahada a Gaza ya karu zuwa 226 tun bayan fara kisan kare dangi kan yankin Ofishin yada labarai na

Adadin ‘yan jarida wadanda suka yi shahada a Gaza ya karu zuwa 226 tun bayan fara kisan kare dangi kan yankin

Ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya tabbatar a yau Juma’a cewa: Adadin ‘yan jaridun da suka yi shahada ya karu zuwa 226, bayan sanar da shahadar dan jarida Ahmed Qaljah.

Ofishin ya bayyana cewa: Yawan ‘yan jaridan da suka yi shahada ya karu zuwa 226 tun farkon yakin kisan kare dangi kan zirin Gaza, bayan sanar da shahadar daya daga cikin ‘yan jaridan Falasdinawa: Ahmed Qaljah, wanda ya yi aiki a matsayin mai daukar hoto na gidan talabijin na Al-Arabiya.

Ofishin ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai hare-haren wuce gona da iri da kashe-kashen kare dang ikan al’ummar Falasdinu da kuma kashe ‘yan jaridar Falasdinawa. Don haka ta jadada yin kira ga kungiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa, kungiyar ‘yan jarida ta Larabawa, da dukkanin kungiyoyin ‘yan jaridu a duniya da su yi Allah wadai da wadannan laifuffuka na yau da kullun kan ‘yan jarida a Falasdinu wadanda suka kasance kwararrun kafafen yada labarai a zirin Gaza.

Ofishin yada labarai na gwamnati ya dora laifukan kisan kare dangin kan gwamnatin mamayar Isra’ila, gwamnatin Amurka, da kasashen da ke da wasu kasashen Turai musamman kasashen Birtaniya, Jamus, da Faransa, da alhakin aikata wadannan munanan laifuka.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments