MDD: Mutane Fiye Da 150,000 Sun Tsere Daga Khan Yunus Saboda Hare-Haren Isra’ila

Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya sun ce kimanin mutane 150,000 ne suka tsere daga kudancin birnin Khan Yunus da ke zirin Gaza tun daga ranar litinin,

Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya sun ce kimanin mutane 150,000 ne suka tsere daga kudancin birnin Khan Yunus da ke zirin Gaza tun daga ranar litinin, a daidai lokacin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai munanan hare-hare a yankin da aka yi wa kawanya.

Louise Wateridge, daga Hukumar Ba da Agaji da Ayyuka ta Majalisar Dinkin Duniya UNRWA, ya bayyana a yau Laraba cewa Falasdinawa sun tsere daga birnin bayan da Isra’ila ta ba da sanarwar cewa su fice daga birnin.

“Sama da kashi 80% na zirin Gaza na karkashin umarnin ficewar dukkanin ko kuma sojojin Isra’ila sun sanya su a matsayin wuraren yaki ,” in ji Wateridge.

Jami’in na Majalisar Dinkin Duniya ya ci gaba da cewa mutane na kaura zuwa Dayr al-Balah da kuma yammacin Khan Yunis, wadanda tuni ke da cunkoson jama’a.

“Suna da matsuguni mai kunci . Da kyar za su iya karbar Karin mutane a wadannan wuraren,” in ji Wateridge.

A waje guda kuma, ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya OCHA ya  bayyana cewa, ta hanyar sanya ido kan yadda jama’a ke tafiya a kasa, ya kiyasta cewa mutane 150,000 ne suka tsere daga Khan Yunis.

Hukumar ta ce mutane da yawa “sun makale a wurin da tuni aka kwashe mazauna cikinsu, ta yadda ta wuya a iya yin wani abu na tallafa musu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments