Gwamnatin Isra’ila Za Ta Fara Yakar Wasu Kasashen Larabawan Yankin Gabas Ta Tsakiya

Bayan Lebanon da Gaza fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila zai fara kai hari kan kasashen Larabawa Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta nakalto

Bayan Lebanon da Gaza fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila zai fara kai hari kan kasashen Larabawa

Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta nakalto daga majiya mai tushe cewa: Gwamnatin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila na shirin tunkarar kungiyoyin gwagwarmayar Musulunci a kasar Iraki, bayan da aka kashe sojojin yahudawa biyu tare da jikkata wasu ta hanyar kai hari da wani jirgin sama maras matuki ciki a yankin Tuddan Julan na kasar Siriya da aka mamaye.

Majiyoyin haramtacciyar kasar Isra’ila sun nakalto daga fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila cewa: Za su duba martanin da ya dace, ko da kuwa ta hanyar kai harin ne da jirgin sama maras matuki ciki domin mayar da martani kan kashe sojojinsu a Tuddan Julan.

Bangarorin Iraki da suka hada da dakarun Hizbullah, Bangaren sojin Sayyidul-Shuhada, da Harkar Nujaba, su ne suka kafa gwagwarmayar Musulunci a kasar Iraki.

A cikin ‘yan watannin da suka gabata, wadannan tawaga na ‘yan gwagwarmaya sun sanar da kaddamar da hare-haren jiragen sama marasa matuka ciki kan yankunan Falasdinu da aka mamaye domin nuna goyon baya ga gwagwarmayar Falasdinawa da kuma goyon bayan al’ummar Gaza.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments