Yakin Gaza Ya Rusa Dukkan Shiri Da Kuma Tunanin HKI A Yankin Gabas Ta Tsakiya Nan Gaba

Tsohon babban kwamandan dakarun IRGC na kasar Iran Mohsen Rezae ya bayyana cewa yakin gaza ko na tufanul aksa ta wargaza dukkan shirin HKI da

Tsohon babban kwamandan dakarun IRGC na kasar Iran Mohsen Rezae ya bayyana cewa yakin gaza ko na tufanul aksa ta wargaza dukkan shirin HKI da kuma tunaninta a gabas ta tsakiya.

Ya ce duk tare da amfani da karfi mafi muni kan al-ummar gaza, tare da kissan Falasdinawa fiye da 47,000 amma ta kasa samun nasara a kansu. Ya kuma zama mata dole ta sulhunta da kungiyar Hamas, wacce a farkon yakin tace sai ta ga bayanta, don dawo da yahudaw 240 da suke tsare a hannuta.

Mohsen Rezae ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon.

Don haka yakin gaza ta maida HKI a matsayin kasa wacce bata da wata mahanga dangane da samuwarta nan gaba ba. Kuma bata san makomarta a yankin ba.

Yace kasa wacce ta kasa kubutar da fursinoninta a Gaza, sai tare da amincewa da sharuddan kungiyar Hamas, wannan ya tabbatar da cewa bata san makomanta a wannan yakin nan gaba ba.

Rezae dai ya na daga kwarraru masu bawa Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae shara a kan al-amuran tsaro, ya na daga cikin dakarun IRGC wadanda suka shiga cikin shirin hare-haren da Iran ta kaiwa HKI a cikin watan octoban shekara ta 2023.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments