Turkiya: Amincewa Da Kasar Falasdinu A Matsyin Yentacciyar Kasa Zai Kara Maida HKI Saniyar Ware

Turkiya: Amincewa Da Kasar Falasdinu A Matsyin Yentacciyar Kasa Zai Kara Maida HKI Saniyar Ware Ministan harkokin wajen kasar Turkiya ya bayyana cewa karuwar yawan

Turkiya: Amincewa Da Kasar Falasdinu A Matsyin Yentacciyar Kasa Zai Kara Maida HKI Saniyar Ware

Ministan harkokin wajen kasar Turkiya ya bayyana cewa karuwar yawan kasashen da suke amincewa da samuwar kasar Falasdinu mai cikeken yanci, musamman daga kasashen Turai zai kara maida HKI saniyar ware a duniya

Kamfanin  dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Turkiyya Hakaan Faidon yana fadar haka a birnin Caracas babban birnin kasar Venezuela a lokacinda yake ganawa da tokwaransa na kasar Iwoon Giil a jiya Alhamis.

Hakaan Faidon ya kara da cewa, lokaci yayi da kasashen duniya zasu amince da kasar Falasdinu a matsayin yentacciyar kasa, kuma idan amincewa da ita ya ci gaba da yaduwa a duniya wannan zai kara maida HKI saniyar ware sannan zai zama mata dole ta amince da abinda mafi yawan kasashen duniya suka amince da shi.

A ranar Laraba  22  ga watan Mayu da muke ciki ne kasashen Norway, Espania da Ireland suka bayyana amincewarsu da kasar Falasdinu a matsayin cikekkiyar kasa mai zaman kanta, wanda ya jawo cece-kuce a tsakanin  kasashen turai da dama.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments