Santocin Amurkan su 8 sun fitar da bayani da a cikin suke yin kira ga gwamnatin Amurka da ta cigaba da bayar da kariya ga sansanin kungiyar ‘yan ta’addar dake kiran kanta: “Mujahidun Khalkh” dake birnin Tirana na kasar Albania.
Sanatocin suna yin kira ne da a bai wa kungiyar kariya alhali a 2010, an shigar da ita a karkashin kungiyoyin ‘yan ta’adda a cikin kasashen Amurka, Canada, da tarayyar turai.
Kiyayya da tsarin jamhuriyar musulunci ta Iran ne dai dalilin da ya sa Amurkan take son yin amfani da kungiyar duk da cewa ma’aikatar harkokin wajenta tana daukarta a matsayin ‘yar ta’adda.
Ita dai wannan kungiyar ta yi wa dubban mutanen Iran kisan kiyashi.