Search
Close this search box.

Iran: Ra’isi Ya Ce: Muna Yi Wa Nahiyar Afirka Kallon Girmamawa Ba Irin Na Bautarwa Ba

Shugaban kasar Iran Sayyid Ibrahim Ra’isi  ya bayyana cewa kallon da kasar Iran take yi wa kasashen Afrika kallon abokan tarayyar ne da kuma girmamawa.

Shugaban kasar Iran Sayyid Ibrahim Ra’isi  ya bayyana cewa kallon da kasar Iran take yi wa kasashen Afrika kallon abokan tarayyar ne da kuma girmamawa.

Kamfanin dillancin labaran IRIB-NEWS na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka a taro na 2 tsakanin JMI da kasashen Afrika  wanda aka gudanar a nan Tehran.  Ya kuma kara da cewa kasar Iran a shirye take ta daga matsayin huldar kasuwanci da tattalin arziki da kasashen Afrika.

A jiya jumma’a 26 ga watan Afrilu ne aka gudanar da taro karo na 2 tsakanin kasashen Afrika da JMI inda wakilan kasashe Afirka kama daga shuwagabannin gwamnatoci, ministocin harkokin kasuwanci, da manya- manyan jami’an gwamnati na kasashen Afirka fiye da 30 suka sami halattar taron.

mataimakin shugaban kasar Zimbawe  Constantino Chiunga wanda da shi da tawagrsa suka wakilci kasar a taron, ya fada wa shugaba  Ra’isi cewa akwai bukatar kasashen biyu su kara fadada dangantakar da ke tsakaninsu fiye da yadda take a halin yanzu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments