Rasha Ta Bukaci Hukumar Nukiliya Ta Kasa Da Kasa Da Ta Kaucewa Zama ‘Yar Koren Kasashen Turai Akan Iran

Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta fada a jiya Laraba cewa; Abinda muke zato daga hukumar makamashin Nukiliya ta

Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta fada a jiya Laraba cewa; Abinda muke zato daga hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa shi ne ta kasance ‘yar ba-ruwanmu a cikin batun da ya shafi siyasa.

Zakharova ta kara da cewa; Akan Iran abinda mu ka tsammata daga hukumar ta makamashin Nukiliya ta kasa da kasa shi ne ta nuna halayyar ‘yar-ba ruwanmu.

Jami’ar diplomasiyyar ta Rasha ta kuma ce; Kungiyoyin kasa da kasa suna da masaniya akan cewa; kasashen yamma ne su ka kawo cikas a cikin yarjeniyar Nukiliyar Iran,amma Tehran a kodayaushe tana nuna cewa a shirye take ta yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta.

A wata hira da shugaban hukumar ta Nukiliya ta kasa da kasa  Rafael Grossi ya yi da kamfanin dillancin labarun Italiya ( ANSA) ya riya cewa Iran ta tara tataccen Uranium da za ta iya sarrafa shi a fagen aikin aikin soja.

Iran din dai ta yi watsi da wannan batu na Grossy,inda shugaban hukumar makamashin Nukiliya ta Iran Muhammad Islami ya ce; ba zai zama karbabbe ba a ce hukumar makamashin ta Nukiliya tana tuhumar Iran,alhali tana kau da kai daga  daya bangaren.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments