Leabanon: Jiragen Yakin HKI Sun Kara Tsananta Yaki A Kudancin Kasar Akalla, Mutane 88 Ne Suka Yi  Shahada A Cikin Sa’o’oi 24 Da Suka Gabata

A sabbin hare haren da jiragen yakin HKI suka kai kan kasar Lebanon, a cikin sa’o’i 24 da suka  gabata, majiyar ma’aikatar lafiya ta kasar

A sabbin hare haren da jiragen yakin HKI suka kai kan kasar Lebanon, a cikin sa’o’i 24 da suka  gabata, majiyar ma’aikatar lafiya ta kasar ta bayyana cewa wannan shi ne hare hare mafi muni tun bayan fara yaki a kan kasar Lebanon.

Tashar talabijin ta Al-Alam a nan Tehran ta nakalto ma’aikatar lafiya ta kasar Lebanon na fadar haka, ta kuma kara da cewa mutane akalla 88 ne suka yi sahada a cikin sa’o’i 24 da suka gabata a kuma yankuna daban daban na kasar. Banda haka wasu mutane 153 sun ji rauni.

Labarin ya kara da cewa jiragen yakin HKI sun kai hare hare masu yawa a yankuna daban daban wadanda suka hada da yankunan Biqa, Jabal Lebanon da sauransu.

Jiragen saman yakin yahudawan sun kai hare hare kan birnin Ba’alabak, Saida, Marja’iyyun, Bintijbail, Jizzeen da sauransu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments