Babban sakataren Majalisar kolin tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Iran na adawa da duk wani sauyi na siyasa a yankin
Babban Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa: Iran na adawa da duk wani sauyi na siyasa a yankin da kuma cutar da alaka tsakanin Iran da Armeniya.
Ali Larijani, babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran, ya gana tare da tattaunawa da Armen Grigoryan, sakataren kwamitin koli na tsaron kasar Armeniya a safiyar yau.
A cikin wannan taro, babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya bayyana gamsuwar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take da shi kan matakin tattalin arziki, siyasa, tsaro da kasar Armeniya, tare da jaddada hadin gwiwa da makwabciyarta ta arewa wajen kammala aikin layin dogo na arewa da kudu da kuma alakanta tekun Farisa da tekun Black Sea.
Ali Larijani ya bayyana goyon bayan Iran ga shawarwarin zaman lafiya tsakanin Armeniya da Azabaijan, inda ya tattauna kan manufar Iran na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, yana mai cewa: Iran a ko da yaushe tana goyon bayan ‘yancin kai da karfin kasashen yankin don kiyaye tsaronsu.
Mr. Grigoryan, sakataren kwamitin koli na tsaron kasar Armeniya, ya bayyana dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu a matsayin wacce ba a taba irinta ba a yayin wannan ganawar, ya kuma bayyana cewa, burinsa na wannan ziyara shi ne fadada huldar dake tsakanin kasashen biyu a dukkan fannoni, ya kara da cewa, “Armeniya a shirye take ta rattaba hannu kan wani cikakken daftari kan huldar abokantaka da Iran nan gaba kadan.”