Search
Close this search box.

Kasar Mali Ta Yi Kira Ga Hadin Kai Tsakanin Kasashen Musulmi Don Warware Matsalar Falasdinawa

Abdoulaye Diop, ministan harkokin wajen kasar Mali ya yi kira ga kasashen musulmi su hada kai don su iya warware matsalar al-ummar Falasdinu. Kamfanin dillancin

Abdoulaye Diop, ministan harkokin wajen kasar Mali ya yi kira ga kasashen musulmi su hada kai don su iya warware matsalar al-ummar Falasdinu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a taron kasashen musulmi karo 15 wanda aka gudanar a birnin Banjul na kasar Gambiya a ranakunan 4-5 na watan mayun da muke ciki.

Ministan ya nuna damuwarsa ga abinda yake faruwa a kasar Falasdinu da aka mamaye, ya kuma bukaci hadin kan kasashen musulmi da farko, sannan sauran kasashen duniya don kawo karshen kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza.

Daga karshe ministan yana ganin samar da kasar Falasdiunu mai zaman kanta, tare da kasar Isra’ila zai iya warware matsala tsakanin al-ummun biyu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments