Kamfanonin jiragen sama kasashen yamma sun bukaci Amurka ta basu izinin ratsawa ko zuwa kasar Iran bayan dakatarwa saboda yakin kwanaki 12 a cikin watan yunin da ya gabata.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto wasu majiyoyin gwamnatin Amurka na fadar cewa a halin yanzu babu wata barazana ta sake komawa yaki da kasar Iran. Sannan jita-jitan da wasu kafafen yada labarai suke yadawa dange da sake komawa yaki da kasar Iran ba gaskiya bane. A cikin yan makonnin da suka gabata ne wasu kamfanonin jiragen saman fasinja na kasashen yamma suka farfado da zirga-zirga zuwa kasar Iran bayan bayan fara yakin watan yuni