Jagora Ya Jaddada Wajabci Daukan Matakan Kalubalantar Zaluncin ‘Yan Sahayoniyya

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Dole ne duniya ta dauki matakin kalubalantar laifukan ‘yan sahayoniyya da magoya bayansu kan zaluncin Gaza Jagoran

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Dole ne duniya ta dauki matakin kalubalantar laifukan ‘yan sahayoniyya da magoya bayansu kan zaluncin Gaza

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, yayin da yake karbar bakwancin dimbin ma’aikata a yau Asabar, a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan “Makon ayyuyka da Ma’aikata” ya bayyana cewa: A yau duniya ta shaida yadda ake daukar manufofin son zuciya kan wasu kasashe.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya ci gaba da cewa daga cikin wadannan manufofi na son zuciya da ake aiwatarwa a yau akwai kokarin mantar da al’umma batun da suka shafi Falasdinawa, yana mai cewa: Kada al’ummar musulmi su kuskura wannan kyale hakan ya faru, domin ko dan bai cancanci a karkatar da hankulan al’umma daga kan al’amuran da halin tsaka mai wuya da Falasdinawa suke ciki a wannan rayuwa musamman ta hanyar yada jita-jita da maganganu iri-iri, ta hanyar bullo da sabbin lamurra da kuma amfani da sabbin kalmomi da ba su da alaka da batun Falastinu, sannan suma Falasdinawan bai kamata a dauke hankulan su muhimman hakkokin da suka doru kansu ba.

Jagoran ya ci gaba da cewa: Laifukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a Gaza na Falastinu, ba wani abu ne da za a yi watsi da shi ba. Dole ne duk duniya ta tsaya kyam wajen kalubantarsa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments