Search
Close this search box.

Iran Ta Karyata  Zargin Da Amurka Da Birtaniya Suka yi Mata Kan Abin Da Ke Faruwa A Tekun Bahar Maliya

A cikin wata wasikar mayar da martani da Jakadan kasar Iran na din-din-din a majalisar dinkin duniya ya aikewa da kwamitin tsaro na Majalisar dinkin

A cikin wata wasikar mayar da martani da Jakadan kasar Iran na din-din-din a majalisar dinkin duniya ya aikewa da kwamitin tsaro na Majalisar dinkin Duniya  ya karyata zargin da  Amaurka da birtaniya suka yi mata na hannun kan abubuwan dake faruwa a tekun bahar maliya da kuma ci gaba da hare haren ramuwa da Kasar Yamen ke kai wa,

Jakadan na kasar Iran Amir Saeid Iravani ya mayar da martani ne game da zargin da kasashen Amurka da Birtaniya suka yi mata a wajen taro da aka yi a ranar 14 ga watan maris, inda ya bayyana cewa wakilan kasashen Amurk da birtaniya sun zargi iran da hannun wajen abin da ke faruwa a tekun bahar maliya kuma ya bayyana zargi a matsayin mara tushe balle madafa,

Haka zalika ya kara da cewa  wata dam ace kasashen biyu suke neman fakewa da ita domin cimma manufofinsu na siyasa da kuma halartar matakin da suka dauka na kaddamar da hari kan kasar Yamen day a sabama dokokin diplomasiyya

Ana sa bangaren jakadan kasar faransa a wajen taron ya bayyana cewa   babban rashin Adalci ne a jingina irin wannan zargin kan kasar iran , daga karshe iran ta bukaci kasar Faransa a matsayin tan a mamba mai kujerar din din din a kwamitin tsaro da ta yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta na taka burki kan yin zargin karya ga kasahen masu yanci  ba tare da wani dalili ba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments