Guterres ya yi kira da a aiwatar da cikakkiyar yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira da a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza tare da sakin fursunoni.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira da a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza tare da sakin fursunoni.

A cewar tashar talabijin ta Aljazeera, Antonio Guterres a cikin wani jawabi da ya yi da ke jaddada wajibcin aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza ya ce: Babu wani abu da zai iya tabbatar da musibar mutuwar Falasdinawa da barnar da yakin Gaza ya haifar.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya yi wadannan kalamai ne a yayin da wasu kafafen yada labaran yahudawan sahyuniya suka wallafa cikakken bayani kan yiwuwar tsagaita wuta da yarjejeniyar musayar fursunoni tsakanin Haramtacciyar Kasar Isra’ila da gwagwarmayar Palasdinawa a zirin Gaza.

A cewar wadannan kafafen yada labarai, an shirya sakin fursunonin yahudawan sahyoniya 3 a rana ta farko, fursunoni 4 na sahyoniyawan a rana ta bakwai, fursunonin sahyoniyawan 3 a rana ta goma sha hudu, da karin fursunonin sahyoniyawan 3 a rana ta ashirin da daya. A rana ta ashirin da takwas za a saki fursunonin yahudawan sahyoniya uku, a rana ta talatin da biyar, wasu uku kuma a mako na karshe za a sako sauran fursunonin sahyoniyawan. Ban da wannan kuma, a kashi na farko na yarjejeniyar, za a sako fursunonin Palastinawa kusan dubu guda, amma ba za a sako fitattun sojojin Hamas da yahudawan sahyoniya suka kama ba a wannan mataki.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments