Shugaban kasar Iran wanda ya karbi bakuncin Fira ministan Pakistan da marecen jiya Litinin, ya bayyana cewa; Kasar Pakistan, makwabciyar jamhuriyar musulunci da muhimmanci, ta dubban shekaru.
Shugaban kasar ta Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda yake Magana a lokacin taron manena labaru na hadin gwiwa da Fira ministan na Pakistan, ya kuma ce; Da akwai haduwar mahanga a tsakanin kasashen biyu akan batutuwa masu yawa da su ka shafi wannan yankin da kuma duniyar musulunci da kuma a fagen siyasar kasa da kasa.”
Shugaba Mas’ud Fizishkiyan ya kuma ce: “A yayin ganawar da mu ka yi da dan’uwana Fira minisan Pakistan da tawagar da taek tre da shi, mun jaddada yadda za a bunkasa alaka ta siyasa, tattalin arziki da al’adu.”
Da yake yin ishara akan aiwatar da yarjeniyoyin da aka kulla a baya a tsakanin kasashen biyu, shugaban kasar ta Iran ya bayyana cewa: Bangarorin biyu za su aiwatar da yarjeniyoyin da su ka kulla a baya, kuma yana cikin abubuwan da mu ka tattauna akai.”
A nashi gefen, Fira ministan na kasar Pakistan Shahbaz Sharif ya yi godiya ga shugaban kasar ta Iran wanda a makwannin da su ka gabata ya kira shi, domin nuna damuwarsa akan halin da ake ciki a yankin-na rikicin kasar da Indiya.”
Haka nan kuma ya bayyana yadda kasar Pakistan ta sami nasara a yakin da ta yi da Indiya, ya kuma ambaci yadda al’ummar kasar ta Pakistan su ka nuna goyon bayansu ga sojojin kasar tasu.
Haka nan kuma bangarorin biyu sun nuna takaicinsu abinda yake faruwa a Gaza, tare da yin kira a kawo karashen yakin da shigar da kayan agaji, haka nan kuma hukunta ‘yan sahayoniyar da su ka tafka laifukan yaki.