Kungiyoyi masu gwagwarmaya da sojojin HKI a yankin yamma da kogin Jordan sun sha alwashin daukar fansar Falasdinawa 4 wadanda sojoji HKI suka kashe, tare da amfani da jirgin yaki wanda ake sarrafashi daga nesa a sansanin yan gudun hijira na Noorush Sham dake kusa da birnin Tulkaram a yankin yamma da kogin Jordan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto ma’aikatar kiwon lafiya ta gwamnatin Falasdina na tabbatar da wannan labarin ta kuma kara da caewa wadanda sojojin suka kai ga shahada a wadannan hare hare sun hada da
Saed Adel Shafi, Nimr Anwar Ahmed Hamarsheh, Mohammad Yaser Raja Shehadeh, da kuma Mohammad Hassan Ghannam Kannoh.