Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: Gaza Tana Cikin Halin Tsaka Mai Wuya  

Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada cewa: Halin da ake ciki a Gaza yana kara muni da zama bala’i Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres

Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada cewa: Halin da ake ciki a Gaza yana kara muni da zama bala’i

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya bayyana halin da ake ciki a Zirin Gaza a matsayin “mai ban tsoro da bala’i”, yana mai gargadin cewa yanayin da Falasdinawa ke fuskanta a yankin na iya zama “manyan laifuffukan yaki na kasa da kasa.”

A cikin jawabin da mataimakiyarsa Amina Mohammed ta karanta a yayin taron “Karfafa ayyukan jin kai a Zirin Gaza”, wanda aka gudanar a birnin Alkahira na kasar Masar a jiya litinin, Guterres ya bukaci al’ummun kasa da kasa da su gina tubalin wanzar da zaman lafiya mai ɗorewa a Gaza da kuma a duk faɗin Gabas ta Tsakiya.

Babban sakataren na Majalisar Dinkin Duniya ya jaddada cewa: Rashin abinci mai gina jiki ya bazu a Gaza ga masifar yunwa da ta tunkaro. Sannan a halin da ake ciki, tsarin kiwon lafiya ya ruguje.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments