Al-Burhan: Huldar Sudan Da Iran Ta Shiga Wani Sabon Mataki

Gwamnatin mulkin soji ta kasar Sudan, ta fitar da wata sanarwa a jiya Lahadi, inda ta ce ma’aikatar harkokin wajen kasar na maraba da sabon jakadan Iran a kasar

Gwamnatin mulkin soji ta kasar Sudan, ta fitar da wata sanarwa a jiya Lahadi, inda ta ce ma’aikatar harkokin wajen kasar na maraba da sabon jakadan Iran a kasar Hassan Shah Hosseini, a gabar da huldar kasashen biyu ke shiga wani sabon mataki.

Shugaban kwamitin ikon mulkin Sudan, kana shugaban rundunar sojin kasar, Abdel Fattah al-Burhan ya karbi takardar nadin sabon jakada na Iran dake kasar a birnin Port Sudan dake gabashin kasar, sannan shugaba Burhan ya yi ban kwana da Abdulaziz Hassan Saleh, sabon jakadan kasar Sudan da zai yi aiki a Iran.

A shekarar 2016, Saudiyya ta yanke huldarta da Iran, kana Sudan da wasu karin kasashen suka bi sahunta.

Amma a ran 9 ga watan Oktoban shekarar 2023, ma’aikatar harkokin wajen kasar Sudan ta fitar da wata sanarwa cewa, an koma huldar diplomasiyya tsakanin kasar Sudan da Iran.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments