Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Martanin Iran Na Gaba Kan Isra’ila Zai Wargaza Isra’ila

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Martanin Iran ga duk wani harin ‘yan sahayoniyya zai kasance mafi tsanani…kuma za su iya gwada aniyar

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Martanin Iran ga duk wani harin ‘yan sahayoniyya zai kasance mafi tsanani…kuma za su iya gwada aniyar Iran din!

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gargadi yahudawan sahayoniyya kan kaddamar da duk wani harin wuce gona da iri kan kasar Iran, yana mai cewa: Martanin da Iran za ta mayar kan duk wani hari da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila za ta kaddamar zai zame mai tsanani da gauni, kuma ga fili ga mai doki.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya fada a yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a birnin Damascus na kasar Siriya cewa: Akwai muhimman batutuwa guda biyu na gaggawa a kan ajandanmu, wadanda suka hada da tunkarar matsalolin ‘yan gudun hijiran kasar Lebanon da suka rasa matsugunansu, da samar da Shirin tsagaita wuta a Gaza da Lebanon.

Araqchi ya ci gaba da cewa: Sun gudanar da tattaunawa mai ma’ana, kuma zasu ci gaba kan batun gabatar da agajin jin kai ga ‘yan gudun hijiran kasar Labanon da tura da kasar Siriya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Martanin Iran kan duk wani harin yahudawan sahayoniyya a fili yake, domin kowane mataki yana da gwargwado irin martaninsa, kuma wannan shi ne abin da Iran ta tabbatar a baya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments