Amurka: Waɗanda Suka Kamu Da Cutar COVID-19 Sun Haura Mutum Miliyan 25

Amurka
ta tabbatar da cewa sama da mutane miliyan 25 ne suka kamu da cutar COVID-19
(Coronavirus) a ƙasar a daidai lokacin da sabon shugaban ma’aikatar fadar White
House na Amurkan ya zargi gwamnatin tsohon shugaban ƙasar Donald Trump da
gazawa wajen samar da rigakafin cutar da ake buƙata.
Wannan
bayani na adadin waɗanda suka kamun yana cikin wata ƙididdiga ce da Jami’ar
John Hopkins ta Amurkan ta fitar kan yanayin yaɗuwar cutar a
Amurkan inda ta ce adadin waɗanda suka kamu a Amurkan ya kai mutane miliyan 25
wanda yake a matsayin kashi 1 cikin huɗu na adadin dukkanin waɗanda suka kamu a
duk faɗin duniya.
A
wata hira da yayi da tashar talabijin ɗin NBC ta Amurkan, shugaban Ma’aikatan
fadar White House ɗin Ron Klain gwamnatin da ta gabatan ta yi riƙon sakainar
kashi ga batun rarraba rigakafin cutar a ƙasar duk kuwa da irin yadda cutar
take yaɗuwa a watannin ƙarshe-ƙarshe na gwamnatin.
Sabuwar
gwamnatin Biden ɗin dai tana fatan
za ta daƙile yaɗuwar cutar ta hanyar rigakafin da za ta raba a ƙasar sai
dai kuma wasu rahotanni suna nuni da cewa akwai kwangaba-kwanbaya cikin yadda
ake raba rigakafin inda a wasu wajejen ma ake fuskantar ƙarancinsu.
015