Search
Close this search box.

Kasashen  Iran Da Pakistan Sun Jaddada Game Da Muhimmancin Kawo Karshen Yakin Gaza Ba Tare Da Sharadi Ba.

A cikin wani bayani na hadin guiwa da kasashen Pakistan da Iran suka fitar sun bukaci dakatar da bude wuta cikin gaggawa ba tare da

A cikin wani bayani na hadin guiwa da kasashen Pakistan da Iran suka fitar sun bukaci dakatar da bude wuta cikin gaggawa ba tare da wani sharadi ba, kuma a bada damar isar da kayan agaji ga alummar gaza da aka mamaye da bawa yan gudun hijara damar komawa gidajensu.

A karshen ziyarar da shugaban kasar Iran Ibrahim Raisi ya kai a kasar Pakistan dukkan bangarorin biyu sun tir da laifukan yaki da Isra’ila ta tafka kan alummar Falasdinu  da kuma killacesu da hana shigar da abinci da magunguna da hakan yayi sandiyar mutuwar falasdinawa da dama,

Daga karshe bangarorin biyu sun nuna goyon bayansu ga duk wani matakin adalci mai dorewa da zai  warware rikicin, bisa mutunta  ra’ayoyin alummar falasdinu, gwamntin Isra’ila bisa goyon bayan Amurka ta yi kisan kiyashi kan alummar Gaza da gabar yammacin kogin Jodan  .  

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments