Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Iran Zuwa Kasar Masar Tare Da Zantawa Da Takwaransa Na Masar

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da takwaransa na kasar Masar a birnin Alkahira Ministan harkokin wajen kasar Iran Sayyid Abbas Araqchi wanda yanzu

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da takwaransa na kasar Masar a birnin Alkahira

Ministan harkokin wajen kasar Iran Sayyid Abbas Araqchi wanda yanzu haka yake kasar Masar ya gana da takwaransa na kasar Badr Abdel Ati a birnin Alkahira na kasar Masar, inda a tattaunawar bangarorin biyu suka fi mayar da hankali kan batutuwan da suka fi muhimmanci a yankin Gabas ta Tsakiya musamman abubuwan da ke faruwa na yaki a Gaza da Lebanon.

Bangaren tattaunawan ya fi mayar da hankali ne kan sabbin abubuwan da suke faruwa a Gaza da Lebanon, inda ministocin harkokin kasashen biyu sun jaddada wajabcin dakatar da laifukan da yahudawan sahayoniyya suke aikatawa kan Falasdinawa, Araqchi a rangadinsa ya zagaya kasashe da suka hada da Lebanon, Siriya, Saudiyya, Qatar, Iraq, Oman da Jordan, tare da ganawa da manyan jami’an kasashen.

Alkahira dai shi ne zango na takwas da ministan harkokin wajen Iran ya kai ziyarar aiki a yankin a wani bangare na yunkurin diflomasiyya na Iran na neman dakatar da yakin Gaza da Lebanon.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments