Search
Close this search box.

Yemen: An Gudanar Da Gagarumar Zanga-zangar Goyon Bayan Falasdinu A Yemen

Tashar talabijin din ‘almasirha’ ta kasar Yemen ta bayar da labarin dake nuni da cewa; Daliban kasar sun yi Zanga-zangar da su ka bai wa

Tashar talabijin din ‘almasirha’ ta kasar Yemen ta bayar da labarin dake nuni da cewa; Daliban kasar sun yi Zanga-zangar da su ka bai wa taken: “Zuriyar da Za a yi fadan karshe da ita.”

Mahalarta Zanga-zangar ta yau sun fitar da bayanin bayan taro da a ciki su ka yi ishara da yadda duniya ta yi shiru wajen  hana ‘yan sahayoniya kisan kiyashi a Falasdinu,tare da yin tir da hakan da kuma dora wa Amurka alhakin cigaba da yakin na Gaza.

Har ila yau, daliban na kasar Yemen sun yi jinjina ga takwarorinsu na jami’o’in  Amurka da  turai suke nuna goyon bayan Falasdinawa.

Daliban na kasar Yemen sun kuma yi kira da a kauracewa sayen duk wata haja kirar ‘yan sahayoniya da masu goyon bayansu.

A gefe daya kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hamas ta fitar da bayani da a ciki take jinjinawa jaruntar “Ansarullah” na kasar Yemen na hana jiragen ruwa zuwa tashishin jiragen ruwan HKI.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments