Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mutane 43 A Jihar Zamfara Na Tarayyar Najeriya Mafi Yawansu Mata Da Yara

Labaran da suke fitowa daga Jihar Zamfara na arewa maso yammacin Tarayyar Najeriya, sun bayyana cewa wasu yan bindiga  sun yi garkuwa ko sun sace

Labaran da suke fitowa daga Jihar Zamfara na arewa maso yammacin Tarayyar Najeriya, sun bayyana cewa wasu yan bindiga  sun yi garkuwa ko sun sace mutane 43 a unguwar Kakidawa na gidan-gona a karamar hukumar Maradun na jihar.

Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto wasu mutanen da basa son a bayyana sunayensu suna cewa, al-amarin ya auku ne a daren Lahadi, da misalign karfe biyu na dare.                                                                                     

Sun kuma kara da cewa hare-haren sun sa, mutane da dama suka shiga daji, amma yan bindigan sun kama mutane 43.  3 daga cikinsu manyan mutane ne, a yayinda saura 40 kuma, sun kasance mata da yara.

Labarin ya kara da cewa yan bindigan sun farwa garin ne a dai-dai lokacinda suke harbi na ‘kan mai uwa da wabi’ kafin ku shiga gida-gida su kama mutane 43.

Majiyar mutanen garin ta bayyana cewa ya zuwa yanzu dai,  yan bindigan basu kira wani ba don jin abinda suke bukata na sako mutanen.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments