Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki

Daya daga cikin manyan-manyan  jami’an gwamnatin tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana cewa: “Babu tantama gwamnatin HK Isra’ila ta tafka laifukan yaki a

Daya daga cikin manyan-manyan  jami’an gwamnatin tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana cewa: “Babu tantama gwamnatin HK Isra’ila ta tafka laifukan yaki a kan Falasdinawa a zirin Gaza da ta killace.

Matthew Miller wanda ya yi aiki a matsayin kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka tun daga 2023 har zuwa karshen gwamnatin Joe Biden, ya fada wa tashar talabijin ta Sky News kan cewa; Isra’ilan ta tafka laifukan yaki.

Da aka yi masa tambaya a kan yakin Gaza a fadar White House, Miller ya ce; An yi ta samun tsabani dangane da yakin, sabani manya-manya wani lokacin kuma kananan sabani, kan yadda za a kare dangantakar  Amurka da HK Isra’ila duk tare da abinda take aikatawa.”. Amma Miller ya tabbatar da cewa HK Isra’ilan ta tafka laifukan yaki wanda babu shakka a cikin hakan..

Da aka tambaye shi a kan, ko me ya sa a lokacin suke Mulki bai bayyana cewa HK Isra’ila tana aikata laufkan yaki ba? Sai ya amsa da cewa:

“Idan mutum yana cikin gwamnati, ba ya bayyana ra’ayinsa na kashin kansa, yana bayyana ra’ayin gwamnatin Amurka ne.”

Haka nan kuma ya ce; Aikin mai magana  da yawun gwamnati, ko dai ka zama mai Magana da yawun shugaban kasa, ko gwmanatin kasar, amma idan baka cikin gwamnati, to za ka iya fadar ra’ayinka.”

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments