Shugaban Kungiyar Hashdushabi Ta Kasar Iraki Ya Ce Dakarun Sa Suna Biyayya Ga Maraji’ai Da Kuma Wanda Ya Taimaka Masu

Faleh Alfayyad Shugaban dakarun Hashdushabi na kasar Iraki ya bayyana cewa dakarun kungiyar suna biyayya ga malaman addini da kuma duk wadanda suka taimaka mata

Faleh Alfayyad Shugaban dakarun Hashdushabi na kasar Iraki ya bayyana cewa dakarun kungiyar suna biyayya ga malaman addini da kuma duk wadanda suka taimaka mata a baya, wajen ganin bayan kungiyar Daesh a kasar. Daga ciki har da JMI.

Kamfanin dillancin labaran IRIB-NEWS na kasa da kasa ya nakalto Fayyad yana fadar haka a lardin diyala a kasar Iraki a yau jumma’a.

Ya kuma kara da cewa dakarun hashdushabia ba zasu taba manta da shahidanta ba daga cikin har da Mahdi Al-muhandis da kuma Shahid kasim Sulamani. Wanda suka bada rayukansu don kafuwar dakarun Hashdu Shabi.

Fayyad y ace, a halin yanzu suna da mayaka wadanda yawansu ya kai dubu 250, kuma a can baya sun sha wahalar samun isassun makamai amma a halin yanzu sun kulla yarjeniya da wasu kamfanoni kera makamai don magance wannan matsalar.

A farkon watan Decemban shekara ta 2020 ne Donal Trump Shugaban Amurka na lokacin sannan wanda zai sake dawowa kan kujerar a cikin kwnaki ma su zuwa, ya bada umurnin a kashe kwamanda rundunar Quds na dakarun IRGC na kasar Iran. Hajja Kasim Sulaimani da kuma Mahdi Al-Muhandis mataimakin rundunar Hashdushabi na kasar ta Iraki.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments