Shugaba Basshar Asad wanda ya karbi bakuncin ministan harkokin wajen kasar Bahrain, Abdullatif Bin Rashid al-Zayyani, bangarorin biyu sun tattauna hanyoyin sake mayar da alaka a tsakaninsu da kuma bunkasa ta, sannan kuma taron labarun kasashen larabawa da za a yi a birnin Manamah na kasar Bahrai a nan gaba.
Bangarorin biyu sun kuma yi musayar ra’ayi akan yadda taron na kasashen Larabawa zai kasance da muhimman abubuwan da zai kunsa.
Tun da kasar Syria ta fada cikin rikici a 2011 Bahrain ta yanke huldar diplomasiyya da ita, sai dai kuma a halin yanzu ta sake bushe shi.