Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan cewa yana kokarin cimma matsaya da kasar Chaina dangane da kamfanin sadarwa da kuma yanar gizo na TIK Tok.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka a shafinsa na ‘Trump Social,
Labarin ya kara da cewa shugaban yana fadar haka a dai dai lokacinda gwamnatin Amurka ta dorawa kayakin kasar China masu shigowa Amurka kudin fito na kasha 125%.
Tun zagaye na farko na shugabancinsa ne shugaban ya fara rigima da kamfanin Tiktok na kasar China wanda ya sami karbuwa a cikin Amurka da kuma kasashen duniya da dama. Amurka tana ganin shafin yanar gizo na tiktok barzane ce ga tsaron kasar Amurka. Kuma har ta bukaci kasashe kawayenta a duniya su daina mafani da Tiktok.
A zangon shugabancinsa na farko dai shugaban ya haramta wayar tafi da gidanka mafi girma a kasar Chaina wato hawawi da kuma kamfanin internet na G%. wadanda yake ganin barazana ne da tsaro da kuma bangaren tattalin arziki ga kasar ta Amurka.