Jagoran harkar musulunci ta Nigeria wanda kamfanin dillancin Labarin Iran na (IP) ya yi hira da shi, ya ti tir da harin dabbancin da Isra’ila ta kai wa Syria, sannan kuma ya ce,manufar harin shi ne aiwatar da mafarkin da ‘yan sahayoniya su ka dade suna yi na mamaye dukkanin yankin, wanda tabbas ba zai tabbata ba.
Jagoran Harkar Musulunci a Nigeria din ya kuma ce; Abinda yake faruwa a Syria ba nasara ce ga al’ummar kasar ba, mamaya ce daga waje, kuma ba za a dade ba za su fahimci cewa suna rayuwa a karkashin mamaya.