Nasrallah: Shugaba Raeisi ya yi imani da lamarin Falasdinu, da gwagwarmayar Falastinawa

Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Hizbullah ta kasar Labanon ya bayyana cewa, marigayi shugaban kasar Iran Ibrahim Raeisi mutum ne mai cikakken imani a fagen siyasar

Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Hizbullah ta kasar Labanon ya bayyana cewa, marigayi shugaban kasar Iran Ibrahim Raeisi mutum ne mai cikakken imani a fagen siyasar  Falasdinu da kuma fafutukar ‘yan gwagwarmaya a yankin.

Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya gabatar a birnin Beirut na kasar Labanon domin nuna girmamawa ga shugaban kasar da mukarrabansa da suka yi shahada a wani hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu a arewa maso yammacin kasar Iran.

Nasrallah ya kuma kira ministan harkokin wajen Iran Hossein Amir-Abdollahian, wanda shi ma ya yi shahada a cikin lamarin da cewa, “mai imani ne da batun gwagwarmaya da yunkurinta.”

Shugaban na Hizbullah ya bayyana wannan lamari a matsayin mai matukar raɗaɗi da bakin ciki a ciki da wajen kasar Iran.

Ya yi nuni da cewa miliyoyin mutane ne suka halarci jana’izar shahidan a fadin Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Sayyid Nasrallah yayin da yake ishara da taron jana’izar marigayi Raisi  ya ce: Taron jana’izar shi ne na uku mafi girma a tarihi, bayan taron jana’izar  Imam Khumaini da kuma Shahid Qassem Soleimani.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments