Larijani:  Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa  Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara

Sakataren Majalisar Koli ta tsaron kasar Iran Dr. Ali Larijani ya bayyana haka ne a  wani sako da ya walalfa a shafinsa na sadarwa dangane

Sakataren Majalisar Koli ta tsaron kasar Iran Dr. Ali Larijani ya bayyana haka ne a  wani sako da ya walalfa a shafinsa na sadarwa dangane da sako fursunonin Falasdinawa da aka yi.

Haka nan kuma ya ce: ‘Yan Sahayoniya sun ga hotunan gagarumar tarbar da aka yi wa Fursunonin Falasdinawan da hakan yake sake tabbatar musu da cewa; Kungiyar Hamas da gwagwarmaya suna da karbuwa da farin jini a tsakanin Falasdinawa bayan gushewar shekaru biyu na kazamin yaki.

A jiya da safe ne dai al’ummar Falasdinu su ka tarbi Falasdinawan da HKI ta sako daga gidajen kurkukunta a karkashin yarjejeniyar kawo karshen yaki da ta kunshi musayar fursunoni.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments