Kungiyar Hamas Ta Ce: Hare-Haren Sojojin HKI A Kan Asbitin Kamal Adwan A Safiyar Yau Laifin Yaki Ne

Kungiyar gwagwaramaya ta Hamas a zirin Gaza ta bada sanarwan cewa kissan kiyashin da sojojin HKI suka aikata a asbitin Kamal Adwan a arewacin Gaza

Kungiyar gwagwaramaya ta Hamas a zirin Gaza ta bada sanarwan cewa kissan kiyashin da sojojin HKI suka aikata a asbitin Kamal Adwan a arewacin Gaza abin yin allawadai ne, kuma laifin yaki ne.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa, a daren jumma’a ne sojojin yahudawan suka farwa asbitin Kamal Adwan, asbiti tilo da ya rage a yankin arewcin gaza, inda suka kashe mutane 53 a cikin asbitin, wadanda suka hada da marasa lafiya likitoci da kuma wadanda suke samun mafaka a cikin asbitin.

Banda haka sojojin yahudawan sun tilastwa kowa barin asbitin daga cikin har da jami’an kiwon lafiya.

A wani labarin da asbitin ya watsa a shafinsa na Telegran ya kara da cewa sojojin yahudawan sun konan dukkan gineginen asbitin ta yadda a halin yanzu babu abinda ya rage mai amfani a cikinsa.

Daga karshe kungiyar ta kammala da cewa gwamnatin HKI da kuma Amurka wacce take tare da ita ne suka da alhakin duk abinda ya faru.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments