Search
Close this search box.

Kasar China Na Goyon Bayan Kasancewar Falasdinu A Matsayin Cikakkiyar  Mamba A Majalisar Dinkin Duniya

Rahotanni sun bayyana cewa Wang Yi ministan harkokin wajen kasar china a sailin taron kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya a birnin NewYork ya fadi

Rahotanni sun bayyana cewa Wang Yi ministan harkokin wajen kasar china a sailin taron kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya a birnin NewYork ya fadi cewa kasarsa tana goyon bayan sanya yankin falasdinawa a matsayin cikakkiyar mamba a kwamitin tsaro na Majalisar dinkin duniya a amatsayin kasa mai cin gashin kanta.

Yace hare haren da Isra’ila  ta kaddamar a yankin gaza ya haifar da mummunan yanayi  ga bil adama kuma kasar china tana kira da a gaggauta dakatar da bude wuta  ba tare da wani sharadi ba, kuma ta bukaci a dauki wasu matakai da zasu taimaka wajen ganin an takaita yi yuwar barkewar rikici a yankin

Idan ana iya tunawa a  baya bayan nan ne hukumar falasdinu ta bukaci kwamitin tsaro ta majalisar dinkin duniya ya sake duba bukatarta ta neman kasancewa mamba  a majalisar, a karon farko a shekara ta 2011 gwamnatin falasdinu  ta gabatar da bukatar ta ta kasancewa mamba mai cin gashin kai a majalisar dinkin duniya   

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments