Iran Ta Yi Tir Da Harin Ta’addancin Isra’ila A Lebanon

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Nasser Kanaani ya bayyana cewa: Harin ta’addancin da aka kai a kasar Labanon an gudanar da shi ne bisa

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Nasser Kanaani ya bayyana cewa: Harin ta’addancin da aka kai a kasar Labanon an gudanar da shi ne bisa tsarin hadakar ayyukan gwamnatin sahyoniyawan sahyoniya da ‘yan amshin shatanta, kuma ya saba wa dukkanin ka’idojin dabi’a da jin dadin jama’a, dokokin kasa da kasa musamman dokokin jin kai na kasa da kasa. kuma dole ne a yi hukunci kan hakan. »

“Wannan ta’addanci, wanda ya zama wani nau’i na kisan gilla, ya sake tabbatar da cewa gwamnatin sahyoniyawan, bata bukatar kwanciyar hanlali da zaman lafiya a yankin.

Ya ci gaba da cewa: Yaki da ayyukan ta’addanci na gwamnatin da kuma barazanar da ke tasowa daga gare su na daukar wani muhimmin lamari, don haka ya zama wajibi kasashen duniya su gaggauta daukar matakin hukunta mahukuntan sahyoniyawa masu aikata laifuka. »

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments