Iran Ta Ce Duk Tare Maida Martanin Da Ta Yi Kan Hukumar IAEA Kan Shirin Nukliya Tana Aiki Tare Da Hukumar

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Aragchi ya bayyana cewa, kasar Iran a shirye take ta maida martani ga duk wata barazana ga shirinta na

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Aragchi ya bayyana cewa, kasar Iran a shirye take ta maida martani ga duk wata barazana ga shirinta na makamashin nukliya, amma kuma a dayan bangaren tana aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta Duniya (IAEA).

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka, a zantawarsa ta wayar tarho da shugaban hukumar makamashin Nukliya Rafael Grossi.

Ministan ya aibata wasu gwanonin hukumar ta IAEA kan matakan da suka dauka kan Iran a taronsu na fasalin da ya gabata, wato na watan Nuwamban wannan shekarar. Ya ce wannan ya sa gwamnatin kasar Iran ta dauki matakan maida martani a kan hukumar. Inda ta sauya na’urorin centrifution da take amfani da su a da, wajen tace makamashin Uranium zuwa wasu sabbi, kuma wadanda suka fi na farkon karfi.

Ya ce kasar Iran a shirye take ta sake komawa teburin tattaunawa da hukumar don warware sauran al-amuran da suka rage, ta ke sabani a kansu da hukumar.

Kafin haka dai babban sakaren hukumar ta IAEA Rafael Grossi ya ziyarci cibiyoyin tace makamashin Uranium na Natanz da Fordow a cikin watan Nuwamban da ya gabata kafin taron gwamnonin hukumar.

Kasashen Burtaniya, Faransa da kuma Jamus ne suka gabatar da korafi dangane da shirin Nukliyar kasar ta Iran a gaban gwamnonin hukumar, inda suka bukaci rahoton na musamman kan shirin Nukliyar kasar ta Iran.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments