Search
Close this search box.

Iran: Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Kasarsa Bata Son Kara Fadada Yakin Gaza

Ministan harkokin wajen kasar Iran Hussain Amir Abdullahiyan ya bayyana cewa kasarsa ko kdan, bata son fafada yakin da ke faruwa a yankin. Kamfanin dillancin

Ministan harkokin wajen kasar Iran Hussain Amir Abdullahiyan ya bayyana cewa kasarsa ko kdan, bata son fafada yakin da ke faruwa a yankin.

Kamfanin dillancin Labaran IRNA na kasar iran ya nakalto Abdullahiyan yana fadar haka a jiya Litinin a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Austria, Alexander Schallenberg a jiya Litinin.

Ya kuma bayyana masa kan cewa hare haren maida martini wanda sojojin Iran suka kai kan HKI a ranar Lahadi, suna bias doka ta kare kai ne wanda doka ta 51 ta MDD ta amince da haka.

Abdullahiyan ya kara da cewa, abinda yake jawo Karin rikici a gabas ta tsakiya shi ne yakin da HKI take fafatawa da Falasdinwa a Gaza da kuma yankin yamma da kogion Jordan.

A na shi bangaren ministan harkokin wajen kasar Austria ya bayyana cewa tashe tashen hankula a yankin Asia ta kudu, zai cutar da kowa ne. Kuma Iran tana da hakkin maida martini kan hare haren da HKI ta kai kan ofishin jakadancnta a birnin Damascus na kasar Siriya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments