Search
Close this search box.

Ana ci Gaba Da Gudanar Da  Zanga zangar Nuna Goyon Bayan Falasdinu A Kasar Birtaniya  

Rahotanni sun bayyana cewa da dubun dubatan alummar kasar birtaniya suka cika manyan titunan birnin London a ranar ta 28 ta gudanar da zanga-zangar yin

Rahotanni sun bayyana cewa da dubun dubatan alummar kasar birtaniya suka cika manyan titunan birnin London a ranar ta 28 ta gudanar da zanga-zangar yin tir da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a gaza  tare kuma da nuna goyon bayan alummar falasdinu da ake zalunta, 

Rahotanni sun nuna cewa masu zanga-zanar da suka fito daga garuruwa daban-daban na birtaniya sun hallar a birnin London ne domin nuna bacin ransu game da ci gaba da kashe mata da yare kanana da Isra’ila ke yi a Gaza,

Babban sakon da masu zanga-zangar suke son aikewa da shi, shi ne neman a gaggauta kawo karshen yakin Gaza  da kuma bada dama  a aike musu da taimakon agaji , da  kuma haramta  aikewa Isra’ila makamai .

Wanann yana zuwa ne adaidai lokacin da aka shiga wata na 7 da HKI ke ci gaba da yin kisan kare dangi kan alummar Gaza  tare da goyon bayan kawayenta Amurka da birtaniya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments