Hamas Ta Ce Ta Hallaka Sojojin Isra’ila da Dama

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta sanar da kashewa, da raunatawa, da kuma kame wasu sojojin Isra’ila, ta hanyar kai musu hari a arewacin zirin

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta sanar da kashewa, da raunatawa, da kuma kame wasu sojojin Isra’ila, ta hanyar kai musu hari a arewacin zirin Gaza.

Abu Obeida, kakakin kungiyar al-Qassam Brigades, reshen soji na Hamas ne ya bayar da wannan bayanin a wani faifan faifan bidiyo yau Lahadi.

Lamarin ya faru ne a yayin wani harin kautan bauna a hanyoyin karkashin kasa a sansanin ‘yan gudun hijirar na birnin Jabalia, in ji shi.

Kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a Gaza tun ranar 7 ga watan Oktoba.

Kusan Falasdinawa 36,000 galibi mata da kananan yara ne suka mutu sakamakon mummunan farmakin da sojoji suka fara tun bayan harin ba zata, da kungiyar Hamas ta kai.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments