Gwamnatin Kamaru Ta Yaye Tsoffin Mayakan Kungiyar Boko Haram Bayan Horaswa Kan Rayuwa Cikin Mutane

Tun shekara ta 2018 ne gwamnatin kasar Kamaru ta bude cibiyoyi guda biyu, don horaswa da kuma dai-daita fahintar addini na ‘ya’yan kungiyar Boko Haram

Tun shekara ta 2018 ne gwamnatin kasar Kamaru ta bude cibiyoyi guda biyu, don horaswa da kuma dai-daita fahintar addini na ‘ya’yan kungiyar Boko Haram kimani 3000 da suka kama.

Har’ila yau da koya masu sana’o’i saboda su sake komawarsu a cikin al-umma.

Shafin yanar gizo na ‘Afrika News’ ya nakalto Evariste Atangana, gwamnan lardin Arewacin kasar Kamaru, yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa: A nan Meri muna da tsoffin mayakan boko haram kimani 3000 wadanda muka sake basu horaswa a cikin wannan cibiyar, sannan a yau mun yaye 600 daga cikinsu, don su sake komawa cikin mutane.

Gwamnan ya kara da cewa: zamu ci gaba da sanya ido a kansu, don tabbatar da cewa sun sauya halayensu da rayuwarsu zuwa yanda ya dace, da gaske.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments