Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu

Fira ministan gwamnatin rikon kwaryar Libiya ya bayyana cewa: Babu wata cibiyar tsaro a Libya sai dai cibiyoyi na yau da kullum da suka hada

Fira ministan gwamnatin rikon kwaryar Libiya ya bayyana cewa: Babu wata cibiyar tsaro a Libya sai dai cibiyoyi na yau da kullum da suka hada da sojoji da ‘yan sanda

Abdul Hamid Dbeibah, shugaban gwamnatin rikon kwaryar gwamnatin hadin kan kasa, ya ce: “Babu wani wuri a kasar Libya, sai dai cibiyoyi na yau da kullum, ciki har da sojoji da ‘yan sanda,” Dbeibah, ya fadi haka ne biyo bayan al’amuran tsaro da suka faru a babban birnin kasar, Tripoli, a ranar litinin bayan kisan Abdul Ghani al-Kikli, wanda aka fi sani da “Ghaniwa,” kwamandan kungiyar da ake kira “Stability Support Apparatus”.

Bayanin na Dbeibah ya zo ne a yayin wani taron tsaro da aka gudanar a makon da ya gabata tare da mukaddashin ministan harkokin cikin gida, Imad al-Tarabulsi, karamin sakatare na ma’aikatar tsaro, Abdul Salam al-Zoubi, da daraktan sashen leken asiri na soji. Mahalarta taron sun ba da cikakken bayani kan matakan aiwatar da shirin tsaro na babban birnin kasar.

Dbeibah ya kara da cewa: “Dukkan sansanonin soji da kayayyakin aiki a kasar dole ne su kasance karkashin ma’aikatar tsaro da sojojin kasar Libya kadai,” yana mai jaddada cewa “babu wata kungiya da ke dauke da makamai a wajen wannan tsarin da ke da hakki, kuma horon hukumomin shi ne ka’idar da ba za a kebe kowa ba.”

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments