Search
Close this search box.

An Kara Gano Karin Kissan Kare Dangin Da HKI Ta Aikata A Asbitin Shifa Na Gaza

Kafafen yada labarai a zirin Gaza sun bayyana Karin ta’asan da sojojin HKI suka kai a kan asbitin Shifa na Gaza, bayan an tono Karin

Kafafen yada labarai a zirin Gaza sun bayyana Karin ta’asan da sojojin HKI suka kai a kan asbitin Shifa na Gaza, bayan an tono Karin gawakin Falasdinawa wadanda suke bisne a karkashin tuddan yashin wadanmda  sojojin suka samar a cikin asbitin a jiya Litinin.

Tashar talabijin ta ‘Al-Jazeera’ ta kasar Qatar ta bayyana cewa an fito da gawakin shahidai Falasdinawa a cikin asbitin a aikin kwace tarin burbushin gine ginen da sojojin HKI suka rusa a cikin asbitin a jiya litinin.

Labarin ya nakalto Isma’ila Athawabitah shugaban bangaren yada labarai na gwamnatin Gaza na fadar haka, ya kuma kara da cewa sojojin HKI sun kashe falasdinawa kimani 400 a cikin asbitin shifa na gaza.

Banda haka labarin ya kara da cewa an gano babban kabarin gama gari na falasdinawan da sojojin HKI suka kashe cikin asbitin.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments