Search
Close this search box.

Amurka Ta Sanyawa Kamfanoni Kasar Iran 2 Da Mutane 4 Takunkuman tattalin Arziki

Ma’aikatar baitul malin Amurka ta bada sanarwan dorawa kamfanoni biyu da kuma mutane 4 takunkuman tattalin arziki, tare da zarginsu da ayyukan barna ta yanar

Ma’aikatar baitul malin Amurka ta bada sanarwan dorawa kamfanoni biyu da kuma mutane 4 takunkuman tattalin arziki, tare da zarginsu da ayyukan barna ta yanar gizo.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ta nakalto ma’akatar baitul malin tana fadar haka a jiya talata ta kuma kara da cewa kamfanonin guda biyu da ma’aikatan kamfin wadanda suke karkashin kula na dakarun kare juyin juya halin musulunci a kasar Iran suna da hannu dumu dumu a wasu hare haren yanar gizo a kan kasar ta Amurka.

Ali-Riza shafi’u, Riza kazimi, Hussain Muhammad da kumai Barodar na daga cikin wadanda takunkuman Amurkan ta shafa, da kuma kamfanoninsu guda biyu.

Tun bayan nasarar Juyin musulunci a Iran a shekara 1979 Amurka take dorawa kasar takunkuman tattalin arziki har zuwa yan zu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments