Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta matsa wa Uganda lamba ta bayyana makomar masu fafutukar kare hakkin bil’adama na Kenya
Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International Kenya ta ƙara matsin lamba ga hukumomin Uganda kan su saki masu fafutukar kare haƙƙin ɗan adam na Kenya Bob Njagi da Nicholas Oyo, waɗanda suka ɓace a babban birnin Kampala, a farkon watan Oktoba. Ana zargin gwamnatin Uganda da Rashin bayyana makomar mutanen biyu.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a yau ranar Litinin, ƙungiyar ta Amnesty International ta kwatanta halin da ake ciki a Uganda a yanzu da mulkin tsohon shugaban ƙasa Idi Amin (1971-1979), wanda aka danganta shi da ɗaya daga cikin mafi munin lokutan take haƙƙin ɗan adam a tarihin ƙasar.