Wani Dan Majalisar Dokoki Na Kasar Rasha Ya Ce Kasashen Yamma Basa Son Samuwar Kungiyar BRICS

Wani dan majalisar dokokin kasar Rasha ya bayyana cewa kasashen yamma basa son samuwar kungiyar tattalin arziki ta BRICS saboda suna son su ci gaba

Wani dan majalisar dokokin kasar Rasha ya bayyana cewa kasashen yamma basa son samuwar kungiyar tattalin arziki ta BRICS saboda suna son su ci gaba da zama shuwagabannin duniya a kan kowa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Konstantin Kosachev yana fadar haka a birnin Mosco ya kuma kara da cewa, a cikin sabuwar duniya da muke cikin zamanin shugabancin wasu yan tsiraru a kasashen yamma ya wuce, daga yanzun mafi yawan kasashen duniya suna bukatar a gudanar da harkokin tattalin arziki, siyasa da zamantakewa a duniya tare, ba tare da nuna bambanci ba.

Kosachev ya kara da cewa mafi yawan kasashen duniya a halin yanzu suna bukatar a dama dasu a harkokin tafiyar da duniya, a mutunta ra’ayinsu, a kuma yi aiki tsakanin kasashen duniya ta hanyar musayar ra’ayi da kuma gamuwa a kan dukkan manya manyan al-amura da suka shafi tafiyar da duniya.

Kungiyar BRICS dai an kafata ne a shekara ta 2000 tsakanin kasashen Barazil, Rasha, Indiya, China da kuma Afirka ta kudu. Kuma manufar kungiyar itace samar da sabuwar duniya wacce kasashen duniya zasu sami zabi a cikin al-amuran tafiyar da duniya. A cikin wannan shekarar ne kungiyar ta tattalin arziki ta BRICS ta kara yawan kasashen kungiyar zuwa 11.

Ana kuma saran nan gaza zata zama abokiyar hamayyar kasashen yamma a cikin al-amura da dama a harkokin tafiyar da duniya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments