Habasha Ta Sanar Da Makoki A Kasar Sakamakon Mutuwar ‘Yan Kasar A Zaftarewar Kasa

Kasar Habasha ta ayyana kwanaki uku na zaman makoki na kasa domin nuna alhini ga mutanen da zaftarewar kasa ta ritsa da su Gidan rediyon

Kasar Habasha ta ayyana kwanaki uku na zaman makoki na kasa domin nuna alhini ga mutanen da zaftarewar kasa ta ritsa da su

Gidan rediyon kasar Habasha “Fana” ya watsa rahoton cewa: Majalisar al’ummar kasar Habasha ta ayyana zaman makoki na tsawon kwanaki uku domin nuna alhini da juyayi ga wadanda bala’in zaftarewar kasa ya rutsa da su a yankin Gezi Gofa da ke kudancin kasar.

Bayanai da suke fitowa daga kasar Habasha suna nuni da cewa: Adadin mutanen da suka mutu sakamakon zaftarewar kasa a Habasha na iya kaiwa mutane 500, a cewar wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar.

Bala’in ya afku ne sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a ranar Litinin da ta gabata a wani yanki mai tsaunuka a kudancin kasar ta Habasha.

Kudancin Habasha dai na fuskantar karancin ruwan sama tsakanin watannin Afrilu da farkon Mayu, wanda ke karuwa a cikin watannin Yuli da Agusta da ke haifar da ambaliya da zabtarewar laka.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments