Mutanen Pakistan Sun Bukaci Gwamnatin Kasar Ta Katse Hulda Da Amurka

Masu zanga zanga daga kungiyoyidaban daban a kasar Pakistan a kuma garuruwa da  birane daban daban sun bukaci gwamnatin kasar ta katse hulda da gwamnatin

Masu zanga zanga daga kungiyoyidaban daban a kasar Pakistan a kuma garuruwa da  birane daban daban sun bukaci gwamnatin kasar ta katse hulda da gwamnatin Amurka saboda tallafawan da take bawa HKI.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran tanakalto masu zanga- zangar suna fadar haka a wasu tarurruka da suka gudanar a garuruwa daban daban don nuna goyon bayansu da kuma yin allawadai da HKI saboda ci gaba da kissan kiyashin da take yi a gaza duk tare da kudurorin MDD da na kutun kasa kasa da suka bukaci ta dakatar da wannan yakin.

Masu zanga zangar sun bukaci gwamnatin kasar Pakikstan ta kaste hulda da Amurka.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments