Aljeriya ta kirayi zaman gaggawa na kwamitin sulhu kan abubuwan dake faruwa a Lebanon

Aljeriya ta yi kira, bisa bukatar Lebanon, da a gudanar da wani taron gaggawa na Kwamitin Sulhu, don yin nazari kan abubuwan da ke faruwa masu hadari a Lebanon, musamman ma babban harin fashewar na’urorin sadarwa. Ministan harkokin wajen kasar Aljeriya Ahmed Ataf ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar Labanon Abdallah Bou […]

Nasrallah: Yahudawa Ba Za Su Koma Arewacin Falastinu Ba Har Sai An Kawo Karshen Yaki Kan Gaza

Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah a ranar Laraba ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka yi shahada ko kuma suka jikkata sakamakon kazamin harin haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar na’urorin sadarwa, inda  Sayyid Nasrallah ya bayyana lamarin a matsayin “babban aikin ta’addanci, aikin kisan kare dangi da kisan kiyashi,” wanda ya kai matsayin […]

Ambaliya Ta Shafi Mutum Miliyan 1.6 A Nijeriya — NEMA

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (NEMA) ta ce kimanin mutane miliyan 1.6 ne ambaliyar ruwa ta shafa a Najeriya tsakanin watan Afrilu zuwa Satumban 2024. Darakta-Janar ta NEMA, Hajiya Zubaida Umar ce ta bayyana hakan a yayin wani bikin koyar da dabarun kariya da ɗaukar matakan gaggawa kan ambaliyar ruwa da aka gudana ranar Alhamis […]

Pezeshkian : Ta Hanyar Hadin Kai Ne, Kasashen Musulmi Zasu Kare Mutuncinsu

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce akwai bukatar musulmi su samar da hadin kai domin kare mutuncinsu da al’ummominsu. Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar a taron makon hadin kan kasashen musulmi na kasa da kasa karo na 38, wanda aka bude jiya Alhamis a birnin Tehran tare […]

Lebanon : Hare-haren Na’urorin Sadarwa Shelanta Yaki Ne, Zamu Mayar Da Martani   

Shugaban kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah ya ce fashe-fashen na’urorin sadarwa da Isra’ila ta kai a ranakun Talata da Laraba, wanda ya kashe mutane 37 tare da raunata kusan 3,000 a Lebanon, shelanta yaki ne. Sayyid Nasrallah ya bayyana hakan a cikin jawabin da ya gabatar da yammacin Alhamis a jawabinsa na farko da aka […]

Labanon : Amurka Da Faransa Sun Bukaci A kai Zuciya Nesa

Amurka ta ce tana kokarin amfani da diflomasiyya domin kauce wa ta’azzarar tashin hankali tsakanin kungiyar Hezbollah da Isra’ila. Mai bai wa shugaban Amurka shawara kan harkokin tsaro, John Kirby ya jaddada kokarin Amurka na yayyafa wa wutar ruwa. Ya kara da cewa abun da Amurka ke yi shi ne kauce wa tashin hankalin, duk […]

IRGC : Isra’ila Za Ta Fuskanci Babban Martani Daga ‘Yan Gwagwarmaya

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar Iran ya ce Isra’ila za ta fuskanci “mummunan martani daga bangaren ‘yan gwagwarmaya” kan ayyukan ta’addancin da ta ke yi a kasar Labanon. A wata wasika da ya aikewa shugaban kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah a jiya Alhamis, Manjo Janar Hossein Salami ya yi Allah […]