Adadin Mutanen Da Suke Ci Gaba Da Kamuwa Da Korona Yana Raguwa A Iran
2020-12-19 20:10:26

Mai Magana da yawun ma’aikatar kiwon lafiya ta Iran, Sima Sadat Lary ta fada a yau Asabar cewa; A cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin wadanda su ka kamu da cutar su ne dubu 6 da 421, wadanda kuma aka kwantar a asibiti su ne; 822.
Danagne da
wadanda su ka rasa rayukansu a cikin sa’o’i 24 da suka gabata kuwa, mai Magana da
yawun ma’aikatar kiwon lafiya ta Iran din ta ce; sun kai 175.
Wannan
adadin ma wadanda suke kamuwa da kuma mutuwa daga cutar ta corona a Iran ya
ragu matuka idan aka kwatanta da makwanni uku da su ka gabata, inda fiye da
mutan dubu 10 su ke kamuwa da ita, wadanda kuma suke mutuwa suke karatar 500 a
kowace rana.
Iran din dai
tana cikin kasashen da suke kokarin samar da allurar riga-kafin cutar ta
corona, inda a halin yanzu aka shiga cikin fagen yin gwaji ga mutane.
Tags:
mutanen da suke ci gaba da kamuwa da korona
yana raguwa a iran
sima sadat lary ta fada a yau asabar
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!